Skip to main content

Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network ta ziyarci Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim a Abuja.

 Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network ta ziyarci Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim a Abuja. 








Hajiya Khadija Bukar Abba Ibrahim, ƴar majalisan tarayya mai wakiltar mazabar Damaturu, Gujba, Gulani da Tarmuwa a karkashin Jam'iyyar APC ta tarbi kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Mairiga a ofis nata dake National Assembly a birnin Abuja. 


A lokacin ziyarar, kungiyar ta mika mata wasikar zama ɗaya daga cikin Patrons nata. Shugaban kungiyar, Hajiya Mairiga ta yabawa Hajiya Khadija akan kekkyawar wakilci da take yiwa mutanen mazabarta tun daga shekarar 2007 har zuwa yanzu. Mairiga ta cigaba da cewa "Kin fitar da mutanen mazabarki kunya a idon duniya, saboda irin ɗaruruwan ayyukan cigaba da kika kawo musu, musamman wajen inganta rayuwar mata da matasa ta fannoni daban-daban"


Akan dalilan kafa kungiyar, Hajiya Mairiga ta ce kungiyar, mata da matasa ne suka assasata don su bada gudumawarsu wa gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baki daya. "Haka zalika, kungiyar ba zatayi ƙasa-a-guiwa ba sai ta tabbatar da duk ƴan takarkarun Jam'iyyar APC tun daga matakin shugaban ƙasa har zuwa ƴan majalisun jaha sunyi nasara a zaɓe mai zuwa don alfarmar Annabi Muhammadu Rasulullahi (S.A.W)". 


Ita kuma acikin jawabanta, Hajiya Khadija tace "na kawo ku cikin ofis ɗina ne don kuzo kuga irin aikin da kuka turo mu muyi muku wannan wuri; shi yasa tun jiya na sanar da duk Jami'an tsaro da ma'aikatan wannan wuri cewa zanyi baƙi daga jaha ta" 


Daga karshe, ta karrama ƴan kungiyar tare da yin alwashin bada gudumawarsa don nasarar Gwamna Mai Mala Buni, Bola Tinubu da duka ƴan takarkarun Jam'iyyar APC daga sama har ƙasa a zaɓe mai zuwa. 


Hajiya Mairiga ta samu rakiyar wasu daga cikin shugabannin kungiyar.


Mustapha Gujba Banker. 


Photo by Arfo.

Comments

Popular posts from this blog

Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.

 Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.  A cikin shiriye-shiriyenta na wayar da kan mutane akan kyawawan manufofi da tsare-tsaren Gwamnatin Mai Mala Buni don su cigaba da marawa Gwamnatinsa da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari, a yau Asabar 24th September, 2022, kungiyar Buni Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta kai ziyara na musamman wa fadan Mai Martaba Sarkin Fika don neman tabarraki da shawarwari . Shugaban kungiyar, reshen Karamar hukumar Fika, Abubakar Ayuba Idriss tare da sauran membobinsa sun samu rakiyar shugaban kungiyar reshen Yobe zone-B Mohammed Musa Kawuwale shima tare da sauran shuwagannin kungiyar na reshen Yobe zone B. A cikin jawabansu, Abubakar Ayuba Idriss da Mohammed Musa Kawuwale sun bayyanawa Mai martaba cewa kungiyar ta fito ne taken ta na "Rama alkhairi da alkhairi' ma'ana, ƙokarin rama alkhairin da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe, m...

Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari.

 Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari. Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Mairiga tana taya mai girma dan majalisar dattija Senata Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a wajen taron karrama ƴan ƙasa da a ake gudanar da ita a babban dakin taro na International Conference Centre, Abuja.  Bikin an shiriya tane don karrama ƴan Nigeria da suke yin ƙokari wajen bada gudumawarsu don tabbatar da zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa, yiwa ƙasa hidima da cigaban Najeria baki ɗaya.  Shugaban kungiyar, Hajiya Mairiga tace "mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan ya cancanci wannan karramawan a wajen shugaban ƙasa Muhammadu Buhari duba ga irin gudumawar da yake bayarwa ta fuskan siyasa, zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa da kawo ɗaruruwan ayyukan cigaban a kasa Najeriya ...

Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.

 Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.  A jiya Asabar, kungiyar Buni Gubana Women and Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Gwamnaty Mairiga ta ziyarci garin Kamfani dake Karamar hukumar Fika don ganawa da mabiya addinin kirista, tayi musu Kira da su marawa Gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari a zaɓen 2023.  Kungiyar ta jaddada musu cewa kar suyi fargaban zaɓen 'Muslim-Muslim' ticket , wato Dan takaran shugaban ƙasa karkashin Jam'iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa Senata Kashim Shettima a zaɓen 2023.  Hajiya Mairiga ta ƙara da tunatar dasu wasu ɗaruruwan ayyukan cigaba da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe a cikin shekaru uku Kachal na mulkinsa, saboda haka tana bukatansu da marawa Gwamnatinsa baya ɗari bisa ɗari don cigaba ayyukan Alheri.  Haka zalika, tayi musu kira da su za...