Skip to main content

Kungiyar Buni Gubana Women & Youth network ta fara shiriye-shiriyen gudanar da manya-manyan tararruka a Yobe zone-A , zone-B da zone-C.

 Kungiyar Buni Gubana Women & Youth network ta fara shiriye-shiriyen gudanar da manya-manyan tararruka a Yobe zone-A , zone-B da zone-C. 







A yau Talata, kungiyar Buni Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Gwamnaty Mairiga ta fara shiriye-shiriyen gudanar da manya-manyan tararruka na ƙaddamar da shugabanninta na Yobe shi'ar gabas, shi'ar kudu da shi'ar arewa. 


Kamar yadda a baya Kungiyar ta ƙaddamar da shugabanninta na jaha, yanzu haka ta fara shiriye-shiriyen ƙaddamar da na shi'oin uku na jahar, daga nan kuma sai na ƙananan hukumomi 17 da gundumomi 178 na Jahar Yobe baki daya. 


Kungiyar, wanda matasa da mata na Jahar Yobe suka hadu suka ƙirkiro da ita don su bada gudumawarsu wa Gwamnatin Mai Mala Buni don ta cigaba da kyawawan manufofin cigaban Jahar Yobe da ta ɗauko kuma mutane suke moran ta a zahiri. Kama daga; ayyukan cigaban matasa da dama, bawa matasa dama a Gwamnatinsa, inganta rayuwar mata-da-yara musamman wajen kiwon lafiya, bada jari da sauran tsare-tsare masu yawa wa mata masu juna, jarirai da yara ƙanana.

Comments

Popular posts from this blog

Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.

 Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.  A cikin shiriye-shiriyenta na wayar da kan mutane akan kyawawan manufofi da tsare-tsaren Gwamnatin Mai Mala Buni don su cigaba da marawa Gwamnatinsa da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari, a yau Asabar 24th September, 2022, kungiyar Buni Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta kai ziyara na musamman wa fadan Mai Martaba Sarkin Fika don neman tabarraki da shawarwari . Shugaban kungiyar, reshen Karamar hukumar Fika, Abubakar Ayuba Idriss tare da sauran membobinsa sun samu rakiyar shugaban kungiyar reshen Yobe zone-B Mohammed Musa Kawuwale shima tare da sauran shuwagannin kungiyar na reshen Yobe zone B. A cikin jawabansu, Abubakar Ayuba Idriss da Mohammed Musa Kawuwale sun bayyanawa Mai martaba cewa kungiyar ta fito ne taken ta na "Rama alkhairi da alkhairi' ma'ana, ƙokarin rama alkhairin da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe, m...

Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari.

 Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari. Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Mairiga tana taya mai girma dan majalisar dattija Senata Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a wajen taron karrama ƴan ƙasa da a ake gudanar da ita a babban dakin taro na International Conference Centre, Abuja.  Bikin an shiriya tane don karrama ƴan Nigeria da suke yin ƙokari wajen bada gudumawarsu don tabbatar da zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa, yiwa ƙasa hidima da cigaban Najeria baki ɗaya.  Shugaban kungiyar, Hajiya Mairiga tace "mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan ya cancanci wannan karramawan a wajen shugaban ƙasa Muhammadu Buhari duba ga irin gudumawar da yake bayarwa ta fuskan siyasa, zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa da kawo ɗaruruwan ayyukan cigaban a kasa Najeriya ...

Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.

 Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.  A jiya Asabar, kungiyar Buni Gubana Women and Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Gwamnaty Mairiga ta ziyarci garin Kamfani dake Karamar hukumar Fika don ganawa da mabiya addinin kirista, tayi musu Kira da su marawa Gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari a zaɓen 2023.  Kungiyar ta jaddada musu cewa kar suyi fargaban zaɓen 'Muslim-Muslim' ticket , wato Dan takaran shugaban ƙasa karkashin Jam'iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa Senata Kashim Shettima a zaɓen 2023.  Hajiya Mairiga ta ƙara da tunatar dasu wasu ɗaruruwan ayyukan cigaba da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe a cikin shekaru uku Kachal na mulkinsa, saboda haka tana bukatansu da marawa Gwamnatinsa baya ɗari bisa ɗari don cigaba ayyukan Alheri.  Haka zalika, tayi musu kira da su za...