Skip to main content

Kungiyar Buni - Gubana Women & Youth Network ta ziyarci Ministan wutan lantarkin Najeria, Engr. Abukakar D. Aliyu a Abuja

 Kungiyar Buni - Gubana Women & Youth Network ta ziyarci Ministan wutan lantarkin Najeria, Engr. Abukakar D. Aliyu a Abuja. 







......Kungiyar ta bashi wasikar zama ɗaya daga cikin Patrons nata, da lambar yabo a bisa ayyukan cigaba da ya kawo wa Jahar Yobe. 


Kungiyar Buni - Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Mairiga ta kai ziyara na musamman ofishin babban Ministan wutan lantarkin Najeria, Engr. Abubakar D. Aliyu (Jarman Potiskum) dake Power House a birnin Abuja. 


A lokacin ziyarar, shugaban kungiyar ta fara da yaba wa Ministan a bisa ƙokari da yakeyi wajen ganin Jahar Yobe ta mori Gwamnatin tarayya da ayyukan cigaba, musamman ayyukan da suke karkashin ofishinsa. 


Hajiya Mairiga ta jaddadawa Ministan cewa kungiyar ta shiriya tsaf domin rama "alkhairi da alkhairi" , ma'ana, kasancewar Gwamnatin Mai Mala Buni ta inganta rayuwar mutanen Jahar Yobe baki ɗaya musamman ta ɓangaren cigaban matasa, mata da yara ƙanana ta fannin kiwon lafiya, Ilimi, raba maƙaman Gwamnati, da sauransu. Saboda haka, kungiyar ta fito da shirin shiga duk lunguna da saƙo na Jahar Yobe don jawo hankulan mutanen biranai na kauyuka don su mara wa Gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari. Haka zalika, kungiyar zata bi duk dabaru da salon kanfen don ganin duk ƴan takarkarun Jam'iyyar APC tun daga shugaban ƙasa har zuwa ƴan majalisun jaha sunyi nasara a zaɓe mai zuwa. 


Shi kuma a cikin jawabansa, Jarman Potiskum ya yaba wa mata da matasan da suka hadu - suka ƙirkiro Kungiyar don nasarar Gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baƙi daya. Ya cigaba da cewa yana bibiyan kungiyar tun daga kafuwarta har zuwa yanzu a kafofin sada zumunta, hankalinsa ta karkata kan kungiyar sosai don irin kyawawan manufofi da tsare-tsare cikin Ilimi da basira da kungiyar ta fito dashi. 


Daga karshe, kungiyar ya mika masa wasikar zama Patron nata tare da lambar yabo a bisa ayyukan cigaba da ya kawo wa Jahar Yobe. 


Singed 

Mustapha Mohammed Gujba.

The Political Banker. 

for Media & Publicity.        


#BUNI_GUBANA_WOMEN_AND_YOUTH_NETWORK

Comments

Popular posts from this blog

Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.

 Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta ziyarci Mai Martaba Sarkin Fika.  A cikin shiriye-shiriyenta na wayar da kan mutane akan kyawawan manufofi da tsare-tsaren Gwamnatin Mai Mala Buni don su cigaba da marawa Gwamnatinsa da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari, a yau Asabar 24th September, 2022, kungiyar Buni Gubana Women & Youth Network reshen Karamar hukumar Fika ta kai ziyara na musamman wa fadan Mai Martaba Sarkin Fika don neman tabarraki da shawarwari . Shugaban kungiyar, reshen Karamar hukumar Fika, Abubakar Ayuba Idriss tare da sauran membobinsa sun samu rakiyar shugaban kungiyar reshen Yobe zone-B Mohammed Musa Kawuwale shima tare da sauran shuwagannin kungiyar na reshen Yobe zone B. A cikin jawabansu, Abubakar Ayuba Idriss da Mohammed Musa Kawuwale sun bayyanawa Mai martaba cewa kungiyar ta fito ne taken ta na "Rama alkhairi da alkhairi' ma'ana, ƙokarin rama alkhairin da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe, m...

Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.

 Muslim-Muslim ticket: Kungiyar Buni Gubana women and Youth Network ta gana da mabiya addinin kirista a Fika, ta kira su da su marawa Jam'iyyar APC baya.  A jiya Asabar, kungiyar Buni Gubana Women and Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Gwamnaty Mairiga ta ziyarci garin Kamfani dake Karamar hukumar Fika don ganawa da mabiya addinin kirista, tayi musu Kira da su marawa Gwamnatin Mai Mala Buni da Jam'iyyar APC baya ɗari bisa ɗari a zaɓen 2023.  Kungiyar ta jaddada musu cewa kar suyi fargaban zaɓen 'Muslim-Muslim' ticket , wato Dan takaran shugaban ƙasa karkashin Jam'iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa Senata Kashim Shettima a zaɓen 2023.  Hajiya Mairiga ta ƙara da tunatar dasu wasu ɗaruruwan ayyukan cigaba da Gwamnatin Mai Mala Buni ta kawo wa Jahar Yobe a cikin shekaru uku Kachal na mulkinsa, saboda haka tana bukatansu da marawa Gwamnatinsa baya ɗari bisa ɗari don cigaba ayyukan Alheri.  Haka zalika, tayi musu kira da su za...

Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari.

 Kungiyar BUNI-GUBANA WOMEN AND YOUTH NETWORK tana taya mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Buhari. Kungiyar Buni-Gubana Women & Youth Network karkashin jagorancin Hajiya Fatima Umar Mairiga tana taya mai girma dan majalisar dattija Senata Ahmad Ibrahim lawan murnan samun karramawa na 'GCON' daga shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a wajen taron karrama ƴan ƙasa da a ake gudanar da ita a babban dakin taro na International Conference Centre, Abuja.  Bikin an shiriya tane don karrama ƴan Nigeria da suke yin ƙokari wajen bada gudumawarsu don tabbatar da zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa, yiwa ƙasa hidima da cigaban Najeria baki ɗaya.  Shugaban kungiyar, Hajiya Mairiga tace "mai girma seneta Ahmad Ibrahim lawan ya cancanci wannan karramawan a wajen shugaban ƙasa Muhammadu Buhari duba ga irin gudumawar da yake bayarwa ta fuskan siyasa, zaman lafiya, hadin kan ƴan ƙasa da kawo ɗaruruwan ayyukan cigaban a kasa Najeriya ...